Ƙasashen Afirka sun naɗa sabbin wakilan wanzar da zaman lafiya a Kongo

Spread the love

Wani taron ƙoli na haɗin gwiwa tsakanin shugabannin ƙasashen gabashi da kudancin Afirka sun naɗa sabbin wakilai domin jagorantar sanya ido kan ƙoƙarin wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo.

Wakilan sun haɗa da tsoffin shugabannin Kenya da Najeriya da Habasha (Uhuru Kenyatta da Olusegun Obasanjo da Hailemariam Desalegn).

Muhimman batutuwan da za su mayar da hankali a zaman lafiyan da ake cigaba da kokarin tabbatarwa sun haɗa da aiwatar da tsagaita wuta cikin gaggawa da sake buɗe hanyoyin shigowa da kaya domin shigo da kayayyakin jinƙai.

Za kuma suyi ƙoƙarin ƙwato filin jirgin sama da ke Goma, ɗaya daga cikin biranen da ƴan tawayen M23 da ke da goyon bayan Rwanda suka ƙwace.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *