Kocin Super Eagles Jose Peseiro ya magantu kan damuwar da ‘yan Najeriya ke nunawa ta rashin buga wasa da kyaftin ɗin tawagar Ahmed Musa ke fama da shi.
Ahmed bai buga ko wasa guda ba cikin huɗu da suka buga a gasar Afcon da ke gudana a Côte d’Ivoire ta 2023.
An Kama Matar Da Ta Sayar Da Kananan Yara 42
Super Eagles za ta kara da Angola bayan cin Kamaru
Amma kocin ya ce duk da rashin buga wasan da Ahmed ke yi yana da amfani a cikin tawagar.
“Zai iya buga wasa, amma abin da mutane ya kamata su sani shi shugaba ne,” kamar yadda Peseiro ya bayyana a taron manema labarai da ake yi idan an kammala wasa.
Super Eagles za ta kara da Angola bayan cin Kamaru
Ya jadda cewa zaman Musa a benci shi kan shi wata dama ce musamman ga matasan ‘yan wasan tawagar, tun da suna yi masa kallon abin koyi.
“Gudunmuwarsa ta kasu kashi biyu, ta cikin fili da kuma ta waje. Idan ba shi da amfani da ba mu kira shi ba tun da fari,” in ji kocin.