Hukumar NSCDC Ta Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Cin Zarafin Karamar Yarinya A Jigawa

Spread the love

Hukumar saron Civil defence ta kasa  reshen jihar Jigawa , ta cafke wani matashi mai suna Mika’ilu Abubakar , mai  shekaru 27  mazaunin  Unguwar ‘YanKoli a kauyen Zakirai dake karamar hukumar Kiyawa ta jahar,  bisa zarginsa da aikata laifin  Fyade ga karamar yarinya mai shekaru 8 a duniya.

Kakakin hukumar tsaron Civil Defence  na jihar  Jigawa ASC Badruddeen Tijjani Mahmud, ne ya bayyan hakan ta cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Alhamis 10 ga watan Oktoba 2024.

Badruddin , ya ce sun sami korafi a ofishin su na garin Kiyawa ta hannun Yayan yarinyar da ake zargin an ci zarafin ta.

Rahotanni na cewa wanda ake zargin ya karbe Jarka yarinyar , har ta bishi zuwa gidansa don ta karba, amma ya aikata mummunar aika-aikar.

Binciken likitoci ya tabbatar da cewa an ci zarafin yarinyar tare ji mata ciwo.

Hukumar ta ce da zarar ta kammala gudanar da bincike za ta gurfanar da shi a gaban kotu don ya fuskanci hukunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *