Ahmad Isa mai gabatar da shirin Rai Dangin Goro ya rasu

Spread the love

Fitaccen ɗan jaridar nan da ya ƙware wajen karanta littattafan adabin Hausa a gidajen rediyo, Ahmad Isa Koko ya rasu.

Wasu daga cikin abokan aikinsa – da suka tabbatar wa BBC labarin rasuwar – sun ce marigayin ya yi fama da doguwar jinya, kafin rasuwarsa yau a birnin Legas da ke kudancin ƙasar.

Ahmad Isa ya kasance ma’aikaci a gidan rediyon muryar Najeriya da aka fi sani da VON.

Marigayin ya yi fice a wani shirinsa mai suna ‘Rai Dangin Goro’ da yake gabatarwa a wasu gidajen rediyo, musamman a Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *