An fara taron ministocin harkokin wajen ƙasashen Ecowas

Spread the love

Ministocin harkokin wajen kasashen mambobin kungiyar Ecowas sun fara taro a yau Alhamis a Abuja, karon farko bayan kasashen Nijar da Mali da Burkina sun sanar da ficewarsu daga kungiyar, yayin da a bangare guda kuma shugaban kasar Senegal, Macky Sall ya dage babban zaben kasar.

Taron Ministocin zai iya zama sharar-fage ga taron da shugabannin kasashen kungiyar za su yi don tunkurar wadannan matsalolin.

Hukumar yaƙi da rashawa ta Kano za ta fara binciken masu ɓoye kayan abinci

Kisan Nafi’u: Kotu ta yi umarnin a duba kwakwalwar Hafsat Chuchu bayan ta yi gum da bakin ta.

Taron, kamar yadda wata sanarwar da kungiyar Ecowas din ta wallafa a shafinta na intanet ta nuna, taro ne na musamman da ya kunshi `yan kwamitin shiga-tsakani da majalisar tsaro a matakin ministoci, wanda sanarwar ta ce za su yi zama da nufin tattaunawa a kan halin da yankin Afirka ta yamma ya samu kansa a ciki ta fuskar tsaro da wasu matsaloli da suka jibanci siyasa.

Tun a ranar 28 ga Janairu ƙasashen Mali da Burkina Faso da Kuma Nijar suka sanar da aniyar ficewa ƙungiyar Ecowas.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *