An gano inda ake sayar da jarirai a Anambra

Spread the love

Gwamnatin jihar Anambra da ke kudancin Najeriya ta ce ta gano wani gidan sayar da jarirai tare da ceto wasu mata masu ciki biyar a garin Umunya da ke yankin karmar hukumar Oyi.

An gano gidan ne a wani sumamen hadin guiwa tsakanin ma’aikatar lafiya da hukumoin tsaron jihar.

EFCC ta gayyaci shugabanin jami’o’in Najeriya da ake karbar kudin makaranatar da dala

Najeriya ta kai wasan ƙarshe a Afcon bayan doke Afirka ta Kudu

Da ya ke bayani ga manema labarai, kwamishinan lafiya a jihar Dr. Afam Obidike ya ce sun gano cewar gidan sayar da yaran na gudanar da harkokinsa ta hanyar basaja a masatyin asibiti, nan kuwa cibiyar safarar jarirai ce.

Ya bayyana sunan gida da “Asibitin Mother Child and Maternity” da ke kan titin jami’ar Tansian, da a Umunya.

Ya ce gidan ba shi da rajista da gwamnatin Anambra, ya na mai na cewar masu aikin jinyar da ke aiki a gidan duk sun tsere.

Kwamishina lafiyar ya kuma ce wadan aka ceto shekarunsu basu ba su wuce 14 zuwa 21 ba. Ya kuma nanata aniyar gwamnan na magance wannan mastala.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *