An kama fiye da mutum 50 kan zargin tayar da zaune-tsaye a Legas

Spread the love

Rundunar ƴansandan Najeriya reshen jihar Legas ta cafke mutum sama da 50 bayan hargitsin da ya kaure tsakanin wasu matasa da ɓatagari a yankin Ile-Epo da ke jihar Legas.

A sanarwar da kakaknin rundunar, SP Benjamin Hundeyin ya fitar ranar Alhamis, babban jami’in ɗansanda yankin ya tura jami’ansa zuwa wajen inda kuma tuni aka maido da zaman lafiya.

Sanarwar ta ce an lalata rumfunan da suke zaune.

Kwamihsinan ƴansanda CP Adegoke Fayoade ya bayar da umarnin a gurfanar da mutanen da aka kama inda kuma ya yi gargaɗi cewa rundunar za ta ɗauki mataki kan duk wanda aka samu da ta da zaune tsaye.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *