An kama matar da ke kai wa Bello Turji makamai a Zamfara

Spread the love

 

Dakarun Rundunar Sojin Operation Fansar Yamma, sun kama wata mata mai shekara 25 a Jihar Zamfara, ɗauke da alburusai 764 da bindigogi guda shida, da ake zargin za ta kai wa ƙasurgumin ɗan bindigar nan, Bello Turji.

A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, an kama matar tare da wani abokin tafiyarta ne a ranar 28 ga watan Disamba, a yankin Badarawa, a Ƙaramar Hukumar Shinkafi.

Wannan na zuwa ne bayan samun rahoton sirri kan safarar makamai daga hanyar Kware zuwa Badarawa.

A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, an kama matar tare da wani abokin tafiyarta ne a ranar 28 ga watan Disamba, a yankin Badarawa, a Ƙaramar Hukumar Shinkafi.

Wannan na zuwa ne bayan samun rahoton sirri kan safarar makamai daga hanyar Kware zuwa Badarawa.

Dakarun sojin sun kafa shingen bincike a hanya, wanda hakan ya kai ga cafke waɗanda ake zargin.

Rundunar ta tabbatar da cewa a halin yanzu ana ci gaba da bincike a kansu domin gano cikakken bayani kan lamarin.

Sanarwar ta ƙara da cewa rundunar tana ƙudurin ganin ta daƙile safarar makamai zuwa hannun ’yan bindiga.

Hakazalika, ta roƙi jama’a su ci gaba da ba da sahihan bayanai domin taimakawa wajen samun nasarori irin wannan.

A baya dai ana zargin wasu mutane suna safarar makamai zuwa hannun ’yan bindigar da ke aikata miyagun laifuka a Zamfara da sauran yankunan Arewa Maso Yamma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *