An Kama Yan Bindiga Dauke Da Kudin Sayan Bindigu A Kano

Spread the love

Rundunar yan sandan jihar Kano, ta samu nasarar kama wasu mutane hudu da ake kyuatata zaton yan bindiga ne, dauke da makamai da kuma kudi , a kan titin By pass dake unguwar Hotoro karamar hukumar Nasarawa ta jihar.

 

Kakakin rundunar yan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne tabbatar da hakan da yammacin asabar, inda ya ce ‘’ jami’ansu ne dake aiki a ofishin yan sanda na Jarkuka,  karkashin jagorancin SP Ahmed Abdullahi ne suka samu nasarar kama su, bayan samun bayanan sirri kan yunkurinsu na shigowa jihar don siyan bindiga kirar AK47.

Wadanda rundunar ta kama sun hada da Shukurana Salihu mai shekaru 25, Rabi’u Dahiru dan shekaru 35, Ya’u Idris mai shekaru 30 dukkansu mazauna jihar Katsina da kuma Muktar Sani mai shekaru 30 mazaunin unguwar Yandodo Hotoro Kano.

 

SP Abdullahi Kiyawa, ya kara da cewa nasarar ta samu ne kamar yadda babban sifeton yan sanda na kasa IGP Kayode Edeolu Egbetokun, yaba su umarnin tabbatar da an kara fadada sintiri a lungu da sako don tabbatar da tsaro a fadin Nigeria.

 

Rundunar ta kama wadanda ake zargin ne a ranar 6 ga watan Maris 2025, da misalin karfe 2:00PM na rana a yunkurinsu na siyan bindigar a cewar SP Abdullahi Haruna Kiyawa.

 

An samu bindigu kirar gida guda 3, harsasai daban-daban guda 12, kwanson harsashi 4, Adda 1, Wukake 4 da Boris  guda 24, wayoyi 4, sai kuma kudi naira miliyan daya da dubu ashirin da takwas da dari takwas do za su sayi bindiga kirar AK47 da su.

Haka zalika rundunar ta tabbatar da cewa yanzu haka ta fara gudanar bincike akansu kuma da zarar ta kamala za ta gurfanar da su a gaban kotu don su fuskanci hukunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *