An kammala bincike kan kisan da aka yi wa masu maulidi a Tudun Biri

Spread the love

Hedikwatar tsaron Najeriya ta ce ta kammala binciken da aka daɗe ana dako kan bam ɗin da aka jefa kan mutane a ƙauyen Tudun Biri a ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna.

Ta kuma ce sojojin da aka samu da laifi a kai harin za su gurfana a gaban kotun soji domin fuskantar hukunci.

Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron, Edward Buba ne ya bayyana haka a taron yaɗa labaran da aka gudanar a Abuja.

A Disambar bara ne wani jirgin sojoji ya jefa bam kan mutanen da ke bikin maulidi lamarin da ya janyo asarar rayuka da jikkatar wasu da dama.

Rundunar sojin Najeriya ta ɗauki alhakin kai harin inda ta ce lamarin ya faru bisa kuskure.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *