An Karrama Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Batun Taimakawa Daliban Dawaki Tofa

Spread the love

Kungiyar Dawakin Tofa Academic Forum (DAF) da gidauniyar ilimi ta Dawakin Tofa (DETFnd) sun karrama Sunusi Bature Dawakin Tofa bisa namijin kokarin da yake yi na ciyar da dalibai gaba a karamar hukumar Dawakin Tofa.

Sunusi Bature wanda shi ne mai magana da yawun gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya samu wannan karramawa ne a wata ziyarar da kungiyar ta kai ofishin sa a ranar Talata.

Kungiyoyin sun yi yabon ne ta wata wasikar godiya da Dr. Mamunu Mustapha ya gabatar a madadin kungiyoyin biyu.

Wasikar ta bayyana yadda Sanusi Bature ya ke bayar da tallafi ga daliban Dawakin Tofa, musamman wadanda suka yi karatun digiri a Jami’ar Bayero Kano (BUK).

Gudunmawar da ya bayar, wanda ya hada da biyan kudaden rajista na Shekarar 2023/2024, ya fitar da dalibai da yawa daga matsalolin kudi, ya ba su damar mayar da hankali kan karatun su.

Baya ga tallafin da yake baiwa daliban BUK, Sunusi Bature ya fadada har zuwa sauran manyan makarantu.

Ya bayar da irin wannan taimako ga daliban da ke karatu a Makarantar Kimiyyar Kiwon Lafiya a Jihar Kano da ke Gwamai, tare da sauran al’amuran da suka shafi cigaban ilimi ga matasa a karamar hukumar.

DAF da DETFnd sun jaddada cewa Sunusi Bature ya jajirce wajen inganta harkokin ilimi a garin Dawakin Tofa ya taimaka matuka wajen ganin an samu karin daliban da suke karatun boko a yankin.

Sun bukace shi da ya ci gaba da kokarinsa na daukaka matsayin ilimi da samar da damammaki ga matasa a cikin al’umma .

Wannan karramawa ta nuna irin gagarumar rawar da shugabanni irin su Sunusi Bature ke takawa wajen ci gaban al’umma .

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *