An karrama yan sanda huɗu saboda ƙin karɓar cin hancin miliyan 8.5 a Taraba

Spread the love

Rundunar ‘yansandan jihar Taraba ta karrama wasu jami’anta huɗu, saboda ƙin karɓar cin hancin naira miliyan 8.5 dagha wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a lokacin da suke aiki a wani shingen binciken ababe hawa.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, David Illoyalonomo ne ya karrama jami’an huɗu a shalkwatar rundunar ‘yansandan jihar.

Mista Illoyalonomo ya ce jami’an sun nuna halin dattako, da ɗaga darajar aikin ɗansanda a idonduniya.

Hukuncin kotu: Yan Kasuwar Magani ta Sabongari a Kano sun rufe shagunansu bayan sun yi sallar Alkunut .

Kano: Wani mtukin Adaidaita sahu ya mayar wa da fasinjan sa wayoyin hannu Iphone 12 promax guda 3 da aka manta.

Kwamishinan ‘yansanda ya ce zai gabatar da jami’an huɗu ga babban sifeton ‘yansanda na ƙasar, Kayode Egbetokun, domin yi musu ƙarin girma da kuma duba yiyuwar karrama su da lambar yabo.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *