An Samu Karin Korafe-korafen Kisan Kai Ta Hanyar Amfani Da Makami Da Kuma Fada Wa Ruwa A Kano.

Spread the love

Rundunar yan sandan jahar Kano, ta bayyana cewa ta samu karuwar korafe-korafen kisan kai da kuma ambaliyar ruwa da yake cinye mutane a fadin jahar.

Kakakin rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanrwar da fitar a ranar Alhamis, a madadin kwamishinan yan sandan jahar CP Salman Dogo Garba.

Sanarwar ta ce rundunar ta yi duba na musamman akan korafe-korafen da ake samu na kisan kai , wanda daga fada sai a chakawa mutum wuka ko kuma tsintar gawar da ruwa ya cinye.

SP Abdullahi kiyawa , ya kara da cewa , wadannan abubuwa suna sanya al’umma cikin damuwa, wanda ya zamo dole a kara sanya ido kan yaya, yara , matasa don nusar da su kan matsaloli.

Cikin shawarwarin da rundura ta bayar sun hada da, a guji duk wani fada ko hada jiki don kaucewa abunda zai haifar da riciki da rigima, haka zalika a guji daukar wani makami da suka hada da Wuka, Gora, Fashasshiyar Kwalaba da kuuma karafa.

Saurari Muryar kakakin rundunar yan sandan Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa

Sannan a kula da wuraren da ake zama duk idan akaga wani makami a dauke shi, domin magance matsalar.

Rundunar ta shawarci matafiya musamman lokacin da ake ruwan sama , a guji shiga ruwa ko tsallake ruwan da ba a san zurfinsa ba.

Kwamishinan yan sandan jahar CP Salman Dogo Garba, ya bayar umarnin fadada bincike a wuraren da ake yawan samun korafe-korafen kisan kai .

A karshe rundunar ta yi kira ga jama’a, a duk lokacin da suka ga wani abu da ba su amince da shi, su gaggauta sanarwa a ofishin yan sanda mafi kusa don daukar matakin da ya dace ko kuma a kira nambar waya kamar haka 08032419754, 08123821575 da 09029292926

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *