An Tafka Muhawara Kan Tambayar Da Wata Budurwa Ta Yi Wa Rundunar Yan Sandan Kano.

Spread the love

 

 

Wasu mabiya shafukan sada zumunta musamman Facebook, sun tafka muhawara, kan wata amsar tambaya da kakakin rundunar yan sandan jahar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya yi bayan wata budurwa, ta nemi shigar da korafin ta kan samarin da suka yiwa yan matansu, alkawarin fitowa don ayi mu su baiko kafin watan Disambar 2024 ya kare, amma ba suka ki fitowa.

SP Abdullahi, ya wallafa tambayar da matashiyar budurwar ta yi masa da cewa” Wata ta tambaye ni wai akwai sashin da ake karbar korafi a Bompai, akan samari wadanda suka ce za su fito kafin Disamba amma ba su fito ba? Amsa: Babu, sai dai a tafi Kotu.

Rundunar yan sandan ta ce babu wani sashi da aka ware don karbar korafin yan mata , kan samarinsu da suka yi mu su alkwarin fitowa don a yi baiko musu baiko, sai dai rundunar ta ce suna damar zuwa kotu don shigar da kararsu.

Wannan wallafa dai ta sanya mutane da dama musamman samari , yin martani kamar haka.

Sagir Danladi Usman Ai ma su wannan tambayar suna da yawa, ni ma zan kai wata yarinya kara taki yadda na fito.

Bashir Sani  Ni kaina akwai wacce nai wa irin wnn alqawarin, yanzu haka na jefa ta a “black list” naje Whatsapp ma na buloke ta. Na tabbatar wnn yarinyar idan ta samu dama zata iya miqani koda barikin sojoji ne.

Sule Ya’u Tariwa  Ya dai kamata a kirkiri Department na musamman. Ko bulala ne a rinka yima samarin shaho, masu cewa sai December.

Nanerh Hawwerh A buɗe musu police ɗin masoya kawai😁

Yahaya Lawan Gadanya  A duba lamarin a daura dakai kafin January

Auwalu Muhd Danlarabawa Zaa cika kotu Kenan da masu wannan laifin
Hafsat A Hussain  Yallabai zaka tsaya min zuwa kotun 🥺🥺

Safiyya M Isa Gama  Bakinku daya da samarin🙄 Idan ba haka ba ai za ka iya daukar mataki.

🏃🏃🏃🏃🏃.

Mohammed Ali Danfulata

Ranka ya daɗe, To Akwai Sashin Kai Ƙarar Masu kaiwa 12:00AM na dare suna chart?

Muazzam Madaki  Hahhhhh😁😁 yadai kamata a duba korafin ta.

Sani Usama Bagari Funtua Officer kufa abokan kowa ne

Kamalu A Muhammad Ranka ya daɗe ba fitowar ce ba sa son yi ba, bata yiwuwa ne saboda halin ƙuncin rayuwar da ake ciki. Gashi kuma mutane sun ɗorawa kansu abubuwan da ba Allah ya ɗora musu ba a kan aure. Mu ragewa kanmu ko ma samu sassauci.

Mubarak Aminu Yakubu

Idan na kama dan sanda ya aikata laifi zan iya kama shi na kawo shi ofishin ku?

Ismail Auwal Sarki

Ai kuwa da an bude a wannan satin cika zeyi taf wajan saboda yawan masu kaho korafin.
Gazali Yakubu Ka aiko ta kotun masoya kawai akwai alkalai.

Bashar Muhammad Dange

Ni dai ina da korafi Abdullahi Haruna Kiyawa a kanon nan wani ya damfare Ni, kuma na san shi, ina number sa, wurin aikinsa sananne ne.
Za a iya taimaka irinmu? Wallahi daga sunan sayen #computer yanzu idan na kira wayarsa baya ɗauka.
Muhammad Bello MAN SAGIR, SUJE HISBA KAWAI WAJEN SHEIKH DAURAWA AKWAI SASHIN ACEN EH.
Husein S. Muhammed Kotun ma dai saidai KOTUN MASOYA.
Luqman Abdullahi Aliyu Gaskiya banaso abude.
Tijjani YusufAjiramu Sidra Ta shiga kasuwar Duniya.
Shafeeu Omar Othman Inda ana kaiwa fa wlh Yammata sai sunfi kowa shan wahala a wannan sabgar 😂😂😂
Abbah Siniya HotoroDa alama dai munci banza yallaboi 😘
Aliyu Abdullahi CisseLallai ya dace ace akwai wannan officer din a bompai saboda a rika hukunta masu shaka tafi 🏌️

Engr Adamu Jarabu

Abdullahi Haruna Kiyawa dama mutum yana iya zuwa kotu direct ba tare da ya kai kara caji ofis sun tura shi kotun ba?
Musa Gimba Yerima Tazo zan hada Mata kem kem dolensa yafito.
Maryam Ibrahim Naala Ya kamata Yan sanda su bude tunda sunche su abokan kowa ne Abdullahi Haruna Kiyawa
Real MD Al-ajab Sai dai mu haɗu a kotun masoya a Dala FM Kano
Hon Sulaiman Amir Rangaza Kaga wata zata tona mana asiri.
ɭɭ King ɭɭAlaramma aduba dai 😂😹💔
Abdul M Baba Aduba lamarinan yallabai 😂🤣

Ali Muhammad Inuwa

 Tsarabar aure tahana yin auren Allah galib.

Khamis Aminu Abdulhamid

Alhamdulillah, Allah yaso babu sashin.

Abubakar Khalid Ak Hussain

Gsky dae ya kamata a duba musu mai gda.
Jibrin Aliyu Uhmm oga muna gdy

Yusuf Muazu Kumo

Nima sai Disamba ko baby 😂❓ Maman Noor

Tahir ITahir

Hhhh 🫰 an bata wuta knn
Umar Alhaji Tasiu Wai idan mutum yarasa yanda zeyi towai yaya zeyi 😦

Ibrahim Alkusawi 

Dakun samar dashi..

Ibrahim Hashim Sa’ad 

Wacce kotun ?
Shu’aibu Nagidan Zango Allah Yasa Mudace Duniya Da Lahira Amen.

Mukhtar Elduniya ShinkafiAsh Sha.

Hakkin Daya rataya akanku ne, ku bi masu Hakkinsu.

Aleeyu Umar Abba

Inna hado muku da court order fa🙄😹👨🏿‍🦯

Zainab Ishaq Muhammad

Maganar gaskia ban ji dadi ba, don har na tattara hujjoji zan kawo sunan wasu mutum 3, duka alqawalin Disamba sukayi min amma shiru😭, daya ma da nayi bincike wai ya tafi Libya neman kudi.

Malam Musa Rafin Kuka

Abdullahi Haruna Kiyawa kace mata Suzo wajanmu mu basu maganin mallaka da bita zai zai.
Faisal Muh’d Sadauki  Zan buɗe Police Station ɗin Masoya saboda nasan za’asamu kuɗi sosai…😂
Usman Shuaib Bosha  Akwae sashin da ake karɓar ƙorafi na kyawawan matan da babu halin kula su?
Aliyu M. Ahmad Idan budurwa ko saurayi ya yaudare ku, za ku iya shigar da ƙara KOTU, a yi musu hukuncin ɗaurin shekara 1, tare da tarar ₦200k a dokar Nijeriya.

MJ Dawanau

Assalamualaikum! Ranka ya dade, a tura su Hisba, Malan Yayi musu nasiha, idan aka dace, sai a daura auren a gaban malam. Domin Ni nasan kudine ya hana su fito. Maza sun daina yaudara, amma suna gudun high bill .

Mugira Yusuf

Kai Jama’a 🤔
Al-Qaseem Abubakar Khaleed  Ya kamata kuwa mu masoya a bude mana police station na masoya 😂

Salisu Abdul

Kotun ma ta Masoya.

Oga Ameenu Ameenu II

Hahhahah Nima Yallah ɓai Abdullahi Haruna Kiyawa
Ina ɗaya daga ciki masu irin wannan al ƙawarin.
Abbah Mustapha Ɗorayi  Allah ya rufa mana asiri babu.

Usman Muhammad Adamu

Gaskiya yakamata A duba wannan Lamari.
Ishaq M Ishaq  Gaskiya yakamata ku bude wannan sashin sai a hada Dana karbar korafi akan Yan matanda suka yaudari samari.

Tanimu Oga Hotoro

🤣🤣🤣🤣 Kan bala’i Gaskiya Yakamata A Bude, Saboda Shigar Da Korafi Kafin aje Kotun.

Ameer Kabeer Maje

Dan Allah Kar anunamusu.

Munir Muhammed

sai wata Disamba.

Bello S Justice

Allah sarki wata tana cikin wani hali.

Koguna Magaji

Muna December BA sai anje kotuba kara basu hakuri saura Kada.

Umar Farouk

Boss. Yakamata a fito da sashin da take magana akai😹.

Muhammad Musa Sale

Follow

Officer Abdullahi Haruna Kiyawa tabbas da kuwa an kama samari da yawa.
Don in mentioned na suna zanyi sati yayi kadan in gama zaiyano sunayensu.
Fatima Ihsan Adam Dole zan kai Aliyu Dahiru Aliyu da Abba Gwale kotu. Sabida sun yaudare ni, sun b’ata min lokaci😩.

Nasir Ibrahim

Yallabai akwai sashin da ake cin abinci amma.
Hamisu Muh’d Dacter  Yalla ɓai Atambayar mana ita idan Mun futo Zata wuce mana gaba ? Abdullahi Haruna Kiyawa.

Gen Sunusi Alhamdulillah Na tsallake rijiya da baya kenan…😵

Zawarawan da nacewa zan fito on December sun fi 5.
Hauwa Saraki  A duba Lamarin ranka y dade.
Fateema Babangida Central Kash officer yakamata aduba lamarin Asamamana.
Anas Idris Shitu Alhamdu lillah munji Dadin wannan Bayanin, i get good Lawyer, but Yallabai Abdullahi Haruna Kiyawa Wanda aka ci Kudinsa ba a Aure sa ba zai iya shigar da Kara Bompai?

Usman Nuhu Abubakar

Oga tunda wannan civil case ne, Ayi mata jagora zuwa Sharia court bamanaki Alkali ya daura musu aure acan Ayi gaba daya a huta
Musbahu Suarjo  Yallabai ai har yanzu December bai kare ba ace mata ta kara hakuri 🤣
Khaleepha Baba Mi’andi  Abdullahi Haruna Kiyawa Yallabai rannan kayi wani shiri kace bell is free amma rannan munje bompai sai da dansanda ya karbi kudi a hannunmu.

Abubakar Basiru Jibaga

Allah mun gode maka, da tuni qila an dasa mana camera ana ka daga murya dakyau, shekarunka nawa ? 😅😃
Queen Meera Dadai an Kara duba lamarin😩Dan tun daga habuja zan kawo nawa korafin kano.

Muhammad Ni’imatullah Aliyu

Yallabai kai da zakai rarrashi ka fadamata kotu!😂

Aliyu Maidoki

Amma Wannan dai yaci amana. Amma baiwar Allah kiyi hakuri Tinubu ne ya Wargaza Mishi shiri 😊😊😊😊.
Kiyi Mishi addua kawai
Bilal Muhammad Bello
Hahhahhaha yakamata ku buɗa wannan sashi gaskiya.

Ummu Safiya S InuwaWan Nan shakiyanci dayawa yake 🤔

Allah yasa su turo cikin disambar din ko bayan disamba.

Ibrahim Shuaibu

Allah ya kyauta 😂😂😂😂😂😂

Salihu Sa’ad Adam

Hahaha Allah yakara lfy sir, amma wannan yar rainin wayoce
Mubarak Musa Baza mu fito din ba, sai an sauke tinibu.
Fateema Kurawa  Ja’iri yasamu wadda ta fishi jarfa🤣😂idan ansan kotun data kai ayi tagging dina.

Saifullahi Abubakar Abdullahi

Abdullahi Haruna Kiyawa yanxu idan ankaimu kotun angama shari’ar aina za’aci abinci 😋🥺🤌
Hamza Imam Kano Rashin sani ne yasa samari ke tsoron aure a shekarun baya, yanzu ne ya kamata aji tsoron aure🤔🙄 dan ko kana da sana’a sai ka haɗa da addu’a👌

Saddika Tsafe

SB Salman zamu hadu dakai sashen kai karar samari mayaudara

Ibrahim Alh Baba KulaAllah sarkin

Wani ya jiƙa mata aiki kenan
Akara hakuri komai lokaci ne.

Sabo Kalaboda Saidu

Toh gaskiya yakamata a bude wannan sashin domin yima yan uwa nisa’u adalci an jima ana yaudarar su da December za’a tura.

Mubarak Sani Muhammad

To Oga a buɗe sashin mana.

Buhari Dalhatu

Anya kuwa 🤔
yallaɓai kodai kaima akwai wacce kayiwa alƙawarinne kake jin tsoro🤣

Abubakar Yusuf Nadabo

Munci banza yasen

Iliyasu Dahiru

Yallabai nima wata ta yaudareni,an daura mata aure jiya ina xankai kokena pls 🙏

Umar Muhammad Jega Muhammad

oga wane hukunci zaku Tanada nan Gaba akan masu yi muku tambaya maras ma,ana?
megirma sp da gaske Ana saida shin kafa da wake a bompai😍

Comr Saifullahi A Bala

A Bude police din masoya mana.

Nuraddeen Abdallah

Gaskiya yakamata asamu wannan sashin domin suma masu yaudara masu lefi ne kuma kune kuke d alhakin kama masu lefi.
Jabir Usman Alsheikh Nifa inajin na Hakura da aure kullum tazara yakemun.
Abban Adawiyya Alharazumy  A matsayin mu Na malamai damu zaku hadasu 😔.
Sadeeque Adam Sardauna  Oga gwara fa a Bude sashin a wajenku don zamu iya sasantawa amma kotu Kuma ana Zama kalau 😲.

Mannir Auwal Maikusa

Watan a baya mata sun yaudari samari son ran su,basu San irin radadin da ake jiba Sai yanzu a Abun ya juya kansu…… Samari Kuna sha’anin ku ama kuji tsoran Allah.

Aliyu Nuhu Sallau

Mai Girma Sp Ina da aboki Mai irin wannan dabi’ar, da ace zaku kokarta duk irin wadannan baragurbin samarin a kama su a antaya su a magarqama ko babu komai gani ga wane zai ishi wane tsoran Allah.

Ali Mukhtar MuhammadAlhmdllh, Babu🙏🙏

AB kaji wata zata jawowa yan kungiya fitina koo.
Idris Kassim Aliyu  Bisa kuɗirin maigirma kwamishinan ‘yansandan jihar Kano CP Salman Dogo Garba, wanda jama’a su ka yi wa laƙani da “Dogon Aiki” kuma kwamishina na arba’in da shida a wannan jiha. Na tabbatar da kiyaye haƙoƙin mutane da hana samari yaudara, to yau dai Allah ya bamu Nasara…. Rahoton da muka samu kan Samarin dake cewa za su fito kafin Disamba, amma yanzu Disambar na neman ƙarewa babu su babu labarin su, dan haka nake cewa wannan case yafi ƙarfin mu sai dai Supreme Court.

Asalin BakatsineMuna Alfahari da wannan jinsin namu👏

Allah yakara doraka akanta kaci gaba da gana mata azaba😋🙏

Zainabu AbuTo akwai sashi masu kula da samari masu zuwa zance empty hand😭😭

Don Allah a temaka ai reffering dina.

Edreeth Hudu Bichi

Gaskiya yallabai a duba lamarin ta wata kila ta kori wasu ne tanatinanin cewa shi zai fito December
Abdullahi Haruna Kiyawa
Yallabai adai duba lamarin.
Usman Giovani  Ya kamata a fara karɓar irin wannan korafin gaskiya.

Kamal S Kamal

Yauwa Alhamdulillah woo🤪 babu Sai wurin alkali

Khadija S Aminu

Yallabai yakamata a Bude sashi na musanman domin hukunta maza mayaudara, aduba wanan koken ranka yadade
Nazirun Jarumi Rano  Haba Yallabai Ai kamatayi Ace akwai sai abunchika daganan idan ba’a tabbatarba sai Aturasu kotu.

Sheikh’

Wai Dan Allah Oga Abdullahi Haruna Kiyawa Abokan aikinku Mata basu haihuwa ne, Allah ban taba ganin macen yar Sanda da Ciki ba …?

Abbas Lastdone

😂😂Yallabai gari ne fa yaci wuta😆 Ni kaina a yanda na tsara da komai ya tafi dai dai Yau 28 December itace ranan daurin aure na amma kaga dai yanda lamarin ya kaya🥹 Yanzu hakama ina kasuwa na zubawa sarautar Allah ifo.

Aliyu Yahaya Isah

Yallabai aiku ya kamata ku karbii korafin daga nan sai ku tura kotun
Ina ganin hakan xaifii.

Suhaib Muhammad In da akwai irin wannan sashe ai da tuni ina Prison, don ni sama da shekaru 10 duk Disamba da alkawari take zuwa min.

Amman ina bawa Mata shawara shi Aure lokaci ne, ku daina takurawa Samari sai sun fito sun aureku wannan ne yasa suke muku ƙarya don a zauna lpy.
Zaharaddeen A Labaran  Ma sha Allah,wato ina cikin alheri dumu-dumu Kenan dan ɗazu aka ɗauramin Aure.
Bukhari Ashafa Yallabai tunda sabuwar shekara zamu shiga a sabbi doka da Za’a fitar ya kamata a saka wannan dan ayi maganin mayaudara.
Sulaiman Yusuf Muhammad  Wannan abu yayi kyau da babu wannan sashen domin kuwa da akwai shi ko shakka babu zai wahala yau na kwana a gida domin kuwa nima nai wa wasu alƙawari.
Muhammad Ghali Baban Zahra Hhhh Ita wanda yace yana sonta taki shi shi kuma ina zai Kaita? Allah ne yake hukuntamu daidai da ayyukanmu Malama.

Comr Ibrahim Muhammad Bangazaa

Mai girma ppro Abdullahi Haruna Kiyawa idan Akai haka duk kullemu za ayi nida abokina Umar Abdullahi Zango

Musa Garba Musa

Shawara zuwa ga folisawa don Allah ku taimaka ku bude sashen da masoya wadanda aka yaudara zasu na kai korafi saboda yan matan nan basu da mutunchi wlh.
Muhammad Salees TK Yakasai Wacce kuma take da saurayi sama da Daya Sedai mu kaisu kotun majalisar Dunkin duniya Dan anan ba za’a Mana Adalci.
Aishat Salisu Isah Dan Allah KO bulala ne a dinga yiwa Yan alqawarin December din nan.

Usman Muhammad

Duk da cewa Yan Sanda sunyi sansani a Kofar Mata tsawon sati 2 ko sama da haka, amma tabbas bayyanar Jami’an Vigilante yau a kofar mata ya kayatar dani matuka, wadda a raina naji cewa Babu wani tsageran Yaron da zae iya wargi don tada hankalin Al’umma.
Saboda da ganin su kasan suma ba kanwar lasa bace, Allah ka zaunar mana da Garuruwan mu lafiya, ka zaunar da Nigeria Lafiya, ka bamu lafiya mai amfani da amfanar wa 🙏
A raina nake furtawa cewa ” Idan ciki bai koshin ba aikin pa ba zae yiwu ba, to yanzu idan sunji yunwa Wa zai basu abinci?” Can kuma nace ” Allah ya kawo wadda zae rika ciyar dasu tsawon lokacin da zasu dauka a wannan sansani don kuwa idan jiki yayi la’asar aikin ma bazae yiwu ba, karshe bacci zae kama mutum ne”.
Abinda Gwamnati take basu baya wadatar dasu da komae.
Allah ka karfafi duk wani mai son ganin al’umma sun zauna lafiya 🙏.

Nura Abubakar

Ai pi taki fashewa ne sir.

Mu’azzam Abubakar Cannavaro

Itama tsokana takeyi yallabai 😅

Sadeeq Guy Son Zage

Suyafe lefe Kawaii zasuga yadda zasu dunga tashi.

Jamilu Ibrahim

Sai kaga yamata ai sai da hali me girma PPRO tunda ba da baki ake ba.. Allah SWT Ya horewa bayinSa.

Khamis Aminu Abubakar Kabo

Yallaboi nima wata baiwar Allah tasani tsaka Mai wuya 😔
Kullum da ita nake tashi daga bacci, Kuma kullum Ina cikin tunanin ta 😭
Inason aurenta Amman tace bazatayi aure yanzu ba 😎
Menene abinda ya dace nayi yanzu 😎.

Abubakar Sadiq Sulaiman

Ya kamata hukumar ‘yan sanda taduba korafin wannan matar.

Ameenu Usman Abubakar

Wanda samarinsu sukayi aure da wanda akawa yan matansu aure da wanda aka dankarowa kishiyoyi duk a hadu a yafi juna Allah ya sanya alkhairi ya bada zaman Lfy😂💔 Duk a hadu a kai zuciya nesa😂😂😂.

Bin Usman Indabawa

Ba laifi samari bane laifin manyan kasarmu ne saboda sun lalata mana gobenmu shiyasa wanyanda suka ce zasu futo disamba suka kasa fitowa.

Murtala Bachirawa

Humm Kawai kudaukesu aikin police xasu bada gudun mawa sosai kafin Allah ya kawo musu wasu.

Abdullahi Muhammad Danhausawa

Ya Kamata a Samu Wannan Sashin Kam domin Ana Cin Zarafin Nisa’u a wannan Sabgar!..💔🚶‍♂️😎

Real Sani Idris

Oga kace Ina daya daga cikin masu zuwa kotu sbd Ina da wannan laifin.

Nafnaf Goron Dutse

Abdullahi Haruna Kiyawa Yallabai Ace Suqara Jira Saura Kadaaaaan Wani Abu Mukejirane😅😅😅

Abubakar Saddiq Ibrahim

Gsky yakamata Aduba lamarin Abuda wannan sashen, Saikuyi bincike Idan kudine yahana mutum fitowa kawai kutaimakai da kudin yafito, Rundunarku agsky tana taimako Kuma tanada kudi, Idankuma kuka gano samarin shahone kiyi Mai buloli.

Alhassan Kmata

Nima zankawo karat tawa kena

Shehu Umar Yunus Wuna

Allah Kabamu Lafiya da Zaman Lafiya, Kano da Nigeria Sune A Gaban Mu, Ka Karawa Yan Sanda Yawan Albashi Su Samu damar Kara Aure

Basheer Muhd Twd

Ranka Yadade Wlh Baku Da Gun Ajiye Masu Wannan Ire Iren Laifikan
Dan Haka Gwara Dakayimata Wayo
Goteeladan Beadwork’s  😂😂😂😂😂😂😂😂nima Akwai Wanda zan kawo a duba lamarin dai😂.

Abba Musa Jiyan

Officer wannan ma laifine ku kuma dama mai laifi kuke nema ,…. Amma ai disambar bai wuceba

Isah Abdu Yaro

Da kamar shekara 2 ne da ta shige da na haɗa ta da wani boka ya tilasta shi ya aure ta a ragowar kwanakin da suka rage sai dai yanzu Allah Ya shiryi bokon ya koma shaye-shaye da sai da wiwi.

Alkasim Ishaq Dukku

Dukkan Yabo ya Tabbata ga Allah Daya tsallakar Dani Tarkon wata Kwaila jarabar Duniya 🙉🙉🙉✍️🏃🏃🏃🏃🏃♥️🏹

Abbas Umar Yahya

Alhmdullih na tsalake rijiya da baya Kenna har naji kirjina yace wani tirissssssss 🤗

Uzairu Halidu Jani Rankai Dade ya kamata ku fara kama Samarin Shaho gaskiya! 🙄🙄🚶

Abdullahi Haruna Kiyawaa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *