Babbar kotun jahar Kano Mai namba 1, dake sakatariyar Audu Bako, karkashin jagorancin Justice Dije Abdu Aboki, ta yankewa Wani Mai suna Ado Idris, hukuncin daurin shekaru 19 , sakamakon samun sa da laifin Yi wa, wata karamar yarinya Fyade.
Mai gabatar da kara, lauyar Gwamnatin jahar Kano , Barista Fatima Ado Ahmed, ta gabatar wa da kotun shaidu guda 5.
A bangaren Wanda Ake tuhumar ya kare Kansa .
Sai dai Mai Shari’ar ta Yi karatun baya, Inda ta yanke masa hukuncin daurin shekaru 19 a gidan ajiya da gyaran hali da tarbiya.
- Mun Samu Umarnin Kotu Na Hana Mu Bayar Da Tsaro A Zaben Kananan hukumomin Ribas: Yan Sanda
- Rundunar Yan Sandan Kano Ta Bankado Wani Korarren Kwansitabul Da Ya Yi Mata Karya A Faifen Bidiyo.