An ƙarkare binciken zargin zubar da ciki da sojojin Najeriya ke yi a asirce

Spread the love

Hukumar kare haƙƙin dan Adam ta Najeriya ta kammala bincike kan zargin da ake yi wa sojojin kasar na gudanar da wani shirin zubar da ciki a asirce.

Wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya wallafa a watan Disambar 2022 ya yi zargin cewa sojojin Najeriya sun zuɓar da cikin mata masu juna biyu 10,000 a yankin arewa maso gabashin kasar, tun daga shekarar 2013.

Rahoton ya ce dayawa daga cikin waɗannan matan an kuɓutar da su ne daga hannun masu iƙirarin jihadi da suka yi garkuwa da su tare da yi musu fyaɗe.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya tattauna da 33 daga cikin matan, inda ɗaya daga cikinsu ta zargi cewa sojojin ne suka zubar musu da ciki ba tare da izininsu ko saninsu ba.

Yan bindiga sun aikata kazamin kisa kan masu shirin buɗa baki a Zamfara

Yawancin Asibitoci A China Sun Fara Dakatar Da Ayyukan Haihuwa

Hukumar kare haƙƙin bil adama ta kasa NHRC ta kafa wani kwamitin da ya fara gudanar da bincike a cikin watan Fabrairun bara.

“Sojoji sun bukaci kwamitin da ya wanke su daga dukkan zarge-zargen da ke ƙunshe a cikin rahoton na Reuters,” in ji NHRC a wani sakon da ta wallafa a shafin X a ranar Talata, yayin da ta sanar da kammala binciken na ta.

Hukumar dai ba ta bayyana sakamakon binciken ba kuma ta ce ba laile ta bayyana sakamakon ga bainar jama’a ba.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ce ya nazarci takardun soji da na asibiti tare da yin hira da shaidu da dama, da suka haɗa da ma’aikatan kiwon lafiya na farar hula da sojoji da jami’an gwamnati da aka ruwaito suna da hannu a shirin zubar da cikin.

Sojojin dai sun musanta rahoton lokacin da ya fara fitowa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *