Anga Karin Jami’an Tsaro A Fadar Sarkin Kano Dake Kofar Kudu.

Spread the love

An ga ƙarin jami’an tsaro a fadar sarkin Kano da ke Ƙofar Kudu a yau Juma’a.

Hakan ya kawo cikas ga zirga-zirga da shige da fice a cikin fadar mai ɗimbin tarihi, inda Sarki Muhammadu Sanusi II ke da zama.

Za a iya ganin jami’an tsaro da kuma motocin tarwatsa masu zanga-zanga waɗanda aka jibge a fadar.

Bayanai sun nuna cewa a yau ne aka tsara cewa Sarki Muhammadu Sanusi II zai yi wa ɗaya daga cikin masu riƙe da sarauta mafi girma a masarautar, Wamban Kano, Mannir Sanusi rakiya zuwa Bichi domin kama aiki a matsayin hakimi.

Sai dai jibge jami’an tsaron ya janyo cikas ga faruwar hakan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *