Atiku ya bayyana damuwa kan ta’azzarar matsalar tsaro a Najeriya

Spread the love

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya sake ɓara dangane da matsalar tsaro da ke ci gaba da addabar Najeriya sakamon ƙarin samun yawan hare-hare da ƴan bindiga ke yi.

Atiku dai ya bayyana rashin jin ɗaɗinsa musamman dangane da garkuwar da aka yi da ƴan jarida da alƙalai da shugabannin ƙwadago da iyalansu a baya-bayan nan.

Tsohon mataimakin shugaban na Najeriya wanda ya bayyana damuwa a shafinsa na X, ya ce ” a wannan lokutan na tashin hankali, ƴan jaridarmu su ne ke haska wa al’umma, kuma ba sa yin ƙasa a gwiwa wajen tabbatar da jagorori sun yi abin da ya kamata. Sai dai kuma abin takaici yanzu su ne ababan kai wa hare-hare.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *