Ayyuka 7 Da Dangote Zai Yi Wa Jami’ar Kano Da Ke Wudil

Spread the love

Shugabannin Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote (ADUSTECH) da ke Wudil a Jihar Kano sun ce an dawo da wutar lantarki a jami’ar a yammacin ranar Juma’ar da ta gabata, bayan tsoma bakin Gwamnatin Jihar da kuma Gidauniyar Dangote.

Wata sanarwa da ta fito daga Shugaban Jami’ar, Farfesa Musa Tukur Yakasai, ya ce, an dawo da wutar lantarkin ce “Sakamakon gaggauta tsoma bakin Gwamnatin Jihar Kano da Uban Jami’ar Alhaji Aliko Dangote ta hannun Gidauniyar Dangote wadda ta biya Naira miliyan 100 a tashin farko inda Gwamnatin Jihar Kano ta yi alƙawarin biyan sauran basussukan da ke kan jami’ar da sauran hukumomi da ma’aikatun jihar.

Farfesa Yakasai ya ce “Gidauniyar Dangote tana duba yiwuwar magance matsalar wutar lantarki a jami’ar ta hanyar samar da wutar lantarki mai aiki da hasken rana.”

Ya miƙa godiyar ɗaukacin ma’aikatan jami’ar kan gaggauta tsoma baki da kuma ƙoƙarin Gwamnan Jihar Abba Kabir Yusuf ta ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar, Dokta Abdullahi Baffa Bichi da kuma Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi Dokta Yusuf Kofar Mata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *