Ba mu da hannu a tashin hankali yayin zanga-zanga a Kano — Ƙungiya

Spread the love

Ƙungiyar Jakadun Zaman Lafiya ta Jihar Kano, sun ce ba su da hannu a ƙone-ƙone da fasa shagunan mutane da aka yi, yayin zanga-zangar yunwa da aka yi a jihar a ranar Alhamis.

Shugaban Kungiyar, Nasiru Usman Naibawa ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Asabar.

Naibawa, wanda tsohon shugaban ƙaramar hukumar Kumbotso ne a jihar, ya ce sun gudanar da gangamin lumana daga ofishinsu da ke Audu Bako Way don gabatar da wasiƙa ga Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero a ƙaramar fada da ke Nassarawa.

Ya ce sun yi niyyar gabatar da irin wannan wasiƙa ga Gwamna Abba Kabir Yusuf, amma suka fasa sakamakon shawarar hukumomin tsaro a jihar.

A cewar Naibawa, shugaba Bola Tinubu yana buƙatar ƙarin lokaci kafin shawo kan ƙalubalen da ƙasar nan ke fuskanta.

Ya yi kira ga masu kishin ƙasa da su daina shiga zanga-zangar da ke gudana wadda ta kai ga karya doka da oda.

Naibawa ya ƙara da cewa babu ɗaya daga cikin mutane sama da 300 da aka kama a jihar da ke da alaƙa da ƙungiyar.

Ya buƙaci Gwamnatin Jihar Kano, da ta daina siyasantar da lamarin tare da mayar da hankali kan harkokin mulki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *