Ba ni da kamfanin tace mai a Malta – Mele Kyari

Spread the love

Shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari ya mayar wa attajirin Afirka Aliko Dangote martani bayan zargin cewa wasu mutanen NNPC sun mallaka kamfanin tace mai a ƙasashen ƙetare.

A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X, Mele Kyari ya yi watsi da zargin inda ya ce ba shi da wani kamfani na tace mai a ƙasashen ƙetare.

A wani bidiyo da ke yawo a kafofin sada zumunta, Aliko Dangote ya yi zargin cewa wasu ƴankasuwar mai da mutanen NNPC sun buɗe kamfanin tace mai a Malta.

“Mun san inda ake wannan aikin kuma mun san me suke yi, ba wai ba mu sani ba,” in ji Dangote.

Da yake mayar da martani, Shugaban NNPC ya ce “ba ni da wani kasuwanci ko wanda ake yi da sunana a ko’ina a duniya idan ba wanda nake yi ba gida na aikin gona.”

“Sanna ba ni da masaniya ko akwai ma’aikacin NNPC da yake da matata a Malta ko wani wuri a sassan duniya.”

Shugaban na NNPC ya buƙaci a fallasa waɗanda Dangote yake zargi tare da sanar da jami’an tsaro domin ɗaukar matakin da ya dace da su.

A cikin bidiyon da ke yawo na Dangote, ya yi zargin ana shigo da man da ba ya da inganci a Najeriya, dalilin ya sa wasu ke samun matsaloli a motocinsu, a cewarsa.

Ya ce idan har ana son tabbatar da gaskiyar abin da yake fada – abin da ya kamata a gudanar shi ne gwaji kan man da ake sayarwa a gidajen mai amma ba daga tashar ruwa ba.

“Wani kawai zai shigo da jirgin ruwa ya gabatar da samfuri da takardar bogi sai a sahale masa – nan gaba za mu ci gaba da magana,” in ji Dangote.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *