Cikin Hotuna Yadda Aka Ci Gaba Da Zanga zanga A Rana Ta 5 A Wasu Jahohin Nigeria

Spread the love

A jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, an samu tsirarun mutane da suka fito zanga-zanga a rana ta biyar da fara ta a sassan kasar.

Duk da cewa an sanya dokar hana fita a jihar, amma an tsinkayi wasu matasa na zanga-zanga a wasu yankunan birnin.

An dai sanya dokar takaita zirga-zirga a fadin jihar bayan da aka samu hatsaniya, to amma gwamnatin jihar ta sassauta dokar daga karfe 8 na safe zuwa 2 na rana.

Sai dai kuma bankuna sun kasance a rufe amma akwai na’urar ATM da ke aiki a wasu bankunan.

Manyan kasuwannin sun kasance a rufe.

Masu baburan a dai-daita suna zirga-zirga amma gidajen mai da dama duk sun kasance a rufe.

Jami’an tsaro kuma na ci gaba da kasancewa a mahimman wurare don dakile abin da ka iya tasowa.

Ga hotuna daga wasu sassan birnin na Kano a yau Litinin:

Yadda masu zanga zanga suka fito a jihar Legas

A rana ta biyar da fara zanga zanga a Najeriya, masu zanga zangar sun sake fitowa kan titunan jihar Legas.

Ga hotunan yadda zanga zangar ta yau ta kasance.

Tinubu ya tabbatar a wani jawabi da aka watsa a fadin kasar a ranar Lahadin da ta gabata cewa gwamnatinsa a shirye ta ke ta saurare da kuma magance matsalolin masu zanga-zangar, yana mai tabbatar da cewa ya ji kiran nasu da babbar murya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *