Cutar kyandar biri na ci gaba da bazuwa cikin sauri a DR Kongo

Spread the love

Hukumomi a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo sun ce cutar Kyandar biri da ta ɓarke na ci gaba da yaɗuwa cikin sauri a ƙasar.

Gwamnatin ƙasar ta ce tana ɗaukar jerin matakai domin yaƙi da yaɗuwar cutar, ciki har da lura da waɗanda suka cuɗanya da masu cutar da kuma ƙara sanya idanu.

Kakkain gwamnatin ƙasar, ya ce mutanen da ake sa ran sun kamu da cutar ya haura 11,000 ciki har da mutum 450 da suka mutu.

Lardin Equateur da ke yammacin ƙasar ne ya fi yawan masu fama da cutar.

A Farkon wannan wata ne Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ayyana cutar a matsayin barazana ga harkokin lafiya a duniya.

A Afirka ta Kudu rahotonni sun ce an samu mutum 20 masu ɗauke da cutar, ciki har da mutum uku da suka mutu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *