DSS Ta Bayyana Dalilin Jibge Jami’an Ta A Fadar Sarkin Kano

Spread the love

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta musanta wasu rahotannin da aka yada na cewa ta jibge jami’an ta a fadar Sarkin Kano, inda ta ce labarin ba gaskiya ba ne.

Daraktan DSS na jihar Kano, Muhammad Alhassan ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Alhassan ya ce hukumar ta DSS ta tura jami’anta zuwa fadar sarkin saboda samar da tsaro sakamakon ziyarar da uwargidan shugaban kasa, Misis Oluremi Tinubu zata kai wa Sarkin.

Ya ce, daga baya an janye jami’a ne biyo bayan dage ziyarar saboda sarkin ba ya gari .

Ya ce babu gaskiya a cikin rahoton da ke cewa jami’an DSS sun yiwa fadar sarkin kano tsinke kan lamarin da ke faruwa a fadar gwamnatin jihar.

Ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da rahoton na karya, wanda ya ce an yi shi ne don haifar ruɗani a cikin al’umma.

A ranar Alhamis ne Majalisar Dokokin jihar ta soke dokar Majalisar sarakunan Kano ta 2019, inda ta rusa masarautun Bichi, Gaya, Karaye da Rano.

Kadaura24

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *