EFCC ta gayyaci shugabanin jami’o’in Najeriya da ake karbar kudin makaranatar da dala

Spread the love

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC, ta kafa wani kwamiti kar takwana a dukkan ofishinta na shiyya a kasar, don dakile biyan kudin makaranta da dala, bayan faduwar darajar da naira ta yi a kasar.

Ta kuma ce ya gayyaci shugabanin jami’o’i masu zaman kansu da sauran manyan makarantu da ke kasar da ake biyan kudin karatun a makarantun da dalar Amurka.

Ƴan sandan sun kama waɗanda ake zargin sun shirya zanga-zanga a Neja

Yan sanda sun harbe dan bindigar da ke addabar Abuja

Wata sanarwa da mai magana da yawun EFCC din Dele Oyewale ya fitar a yau Laraba ya ce kwamintin na kar ta kwana zai tabbatar da ganin an bi dokar hana lalata kudin kasa da amfani da dala a tattalin arziki.

Sanarwar ta kuma ce shugaban hukumar Ola olukoyede, wanda ya kaddamar da kwamitin kar ta kwana a Abuja, ya ce manufar smar da wannan kwamitin shi ne kare yadda ake cin zarafin tattalin arziki, da dukkan wasu wurare da kudde ke zurarewa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *