ami’an hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa, EFCC ta shiyyar Uyo sun kama wasu mutum 40 da ake zargi da damfara ta intanet a wani samame da suka yi da safiyar yau, Juma’a a wurare biyu daban-daban a jihar.
Hukumar ce ta sanar da hakan a shafin sada zumuntata na X.
Mutum 21 daga cikin mazan da ake zargin an kama su ne a garin Eket, yayin da sauran mutum 19 kuma a a Ikot Ekpene aka kama su.
Kayayyakin da aka ƙwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da mota guda ɗaya da kwamfutocin tafi-da-gidanka guda tara da wayoyi 64 da kuma agogo mai kaifin basira
Hukumar ta ce za a gurfanar da su gaban kotu bayan kammala bincike.
- Yan Sanda Sun Gargadi Jama’a Su Guji Yada Labaran Karya Cewar Sarkin Kano Na 15 Zai Yi Sallah A Kofar Kudu
- An samu lauyan da zai kare mutumin da ya cinna wa masallaci wuta a Kano