‘Fursunonin da ke jiran shari’a a Najeriya sun kai 48,932’

Spread the love

 

Hukumar kula da gidajen yari ta Najeriya ta yi kiran a samar da tsari mai kyau da zai rage yawan cunkoso a gidajen yarin ƙasar, inda yanzu haka yawan fursunonin da ke jiran shari’a ya kai 48,932.

Da yake jawabi a wani taron tattaunawa da jami’an hukumar a ranar Litinin, muƙaddashin shugaban hukumar kula da gidajen yarin ta Najeriya, Sylvester Nwakuche, ya ce cunkoson da ake fama da shi a gidajen yarin ƙasar ya zama babbar barazana ga aikin su.

CSC Musbahu Lawan Ƙofar Nasarawa, shi ne kakakin hukumar gidan yarin reshen jihar Kano, ya ce lallai gidan yarin suna cikin wani hali, inda ya ƙara da cewa akwai buƙatar a samar da tsari mai kyau domin rage cunkosun.

BBCH

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *