Gobara Ta Ci Ofishin ’Yan Sanda A Kano

Spread the love

Gobara ta tashi a Babban Ofishin ’yan sanda da ke unguwar Dakata a Karamar Hukumar Nassarawa a Jihar Kano.

Kwamishinan yan sandan jihar, CP Muhammed Usaini Gumel, ya ce gobarar ta safiyar Litinin, “ta kone wani bangare gaba daya a babban ofishin ’yan sandan da ta tashi.

“Amma duk haka, babu abin da ya sami makaman da ke ofishin.”

karan ta wannan labarin Hukumar Karbar Koke-Koke Ta Rufe Rumbunan Abinci 5 A Kano

karan ta wannan labarin Zamu gayyaci masu zuba hannun jari dan bunkasa tattalin arzikin masarautar Kaltungo da Jihar Gombe:sarkin Kaltungo

Kwamishinan ’yan sandan ya ce tashin gobarar ke da wuya, jami’an hukumar kashe gobara ta jihar suka zo suka kashe ta, kuma ana bincike don gano musabbabin tashinta.

“An killace wurin domin hana masu kallo da miyagu shiga, kuma DPO na yankin yana kan tantance wasu takardun da abin ya shafa,” inji shi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *