Wata gobara ta tashi a kasuwar Karu – da ke Abuja babban birnin Najeriya – da aka fi sani da tsohon Karu.
Shaidu sun ce gobarar da ta tashi da maraicen ranar Alhamis ta yi sanadiyyar asarar dukiya mai tarin yawa.
Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba.
Tuni dai ma’aikatan kashe gobara ke ƙoƙarin kashe wutar da ta tashi a kasuwar.