Gumurzu tsakanin ƴanbindiga ya kai ga kisan gaggan ƴanfashin dagi a Zamfara

Spread the love

Rahotanni daga jihar Zamfara da ke arewa-maso-yammacin Najeriya na cewa akalla fitattun shugabannin ‘yan bindiga biyar ne aka kashe.

Hakan ya faru ne a yayin wani rikici da ya barke a tsakanin mayakan Dogo Bali da Kachalla Mai ‘Yankuzo, abun da ya yi sanadiyyar halakar gwamman mayaƙan tare da jikkata wasu da dama.

Rahotannin na cewa bangarorin ‘yan bindigar sun gwabza fada ne a ranar Lahadi a garuruwan Mada da Munhaye da kuma a ‘Yan awaren Daji, dukansu a ƙaramar hukumar Mulki ta Tsafe da ke jihar Zamfarar.

Rahotanni sun ce rikicin ya kazance har ya kai ga wani ɓangare na Makama da tawagarsa suka nufi dazukan Hayin Allhaji da Munhaye da ke karamar hukumar Mulki ta Tsafe domin daukar fansar Dogo Bali da aka kashe.

Ma su hakan Kabari sun roki gwamnatin Kano ta fara biyan su Alawus

EFCC ta ƙwato naira biliyan 60 a cikin kwana 100 – Olukoyede

A can ne suka hadu da daruruwan mayaƙan Ado Aleru da suka yi musu kwanton ɓauna kuma aka kashe da dama daga cikinsu.

Daga cikin gaggan shugabannin ‘yan bindigar da mayaƙan Aleru suka kashe har da waɗanda ake yi wa laƙabi da ƊanMakaranta da Malam Gainaga, da Mallam Tukur da Malam Jaddi.

Mai Magana da yawun hedikwatar tsaron sojin Najeriya, Birgediya Janar Tukur Gusau, ya tabbatar wa da BBC aukuwar gumurzun.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *