Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Sauke Shugaban Hukumar Tara Kudaden Shiga Daga Mukaminsa

Spread the love
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin Dr. Zaid Abubakar a matsayin sabon shugaban hukumar tara haraji ta jihar Kano (KIRS).
Gwamnan ya kuma amince da nadin Kassim Ibrahim a matsayin daraktan zartarwa na hukumar tara kudaden shiga.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce sabon tsarin gudanarwar zai fara aiki nan bada dadewa ba yayin da tsohon shugaban hukumar tattara kudaden shiga na jihar Kano Alh. Sani Abdulkadir Dambo ya koma aiki a matsayin mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin zuba jari.
ALHEEKMAH.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *