Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya dakatar da kwamishinan ayyuka na musamman, Auwalu Danladi Sankara bisa zargin da hukumar Hisba ta jihar Kano ta yi masa na ”lalata da wata matar aure”.
Cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim, ya fitar ya ce an ɗauki matakin ne domin samun damar gudanar da cikakken bincike kan zargin da ake yi wa kwamishinan.
Ya ce za a gudanar da bincike domin tabbatar da gaskiya da kuma kare martabar gwamnatin jihar.
A ranar juma’a ne dai hukumar Hisba ta jihar Kano ta fitar da sanarwar kama kwamishinan bisa zarginsa da mu’amala da matar aure a wani gida da ba a kammala ba, a jihar Kano.
“Muna ɗaukar duka zarge-zargen da muhimmanci kuma za mu yi bincike da nufin fito da gaskiya domin duka ƴan jihar Jigawa su gani,” in ji sakataren gwamnatin jihar.
Ya kuma ce an ɗauki matakin dakatar da kwamishinan ne domin yin sahihin bincike da kuma yin adalci ga kowane ɓangare.
Sanarwar da gwamnatin ta fitar, ta ce abin kunya ne abin da ake zargin kwamishinan da aikatawa kuma cin fuska gare ta.
Tuni kuma gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti mai mambobi huɗu waɗanda za su yi bincike da kuma gabatar da rahoto cikin mako biyu kacal.
BBCH