Yanzu haka gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya rantsar da sabbin Alƙalai a matakan kotunan daban-daban na jihar ta Kano.
Hakan na zuwa ne ta cikin wata sanarwa da babban daraktan yaɗa labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a yau Juma’a, da aka aikewa manema labarai.
Sanarwar ta ce Alƙalan da Gwamnan Kano ya rantsar sun haɗar da Alƙalan Babbar kotun Jiha guda tara (9), da kuma Alƙalan kotun ɗaukaka ƙara na shari’ar Musulunci guda uku (4), bayan da hukumar kula da sharia ta kasa (NJC) da kuma majalisar dokokin jihar Kano suka amince da naɗin nasu.
Haka kuma waɗanda aka naɗa a matsayin alƙalan babbar kotunan Jihar sune, Justice Fatima Adamu, Justice Musa Ahmad, Justice Hauwa Lawan, da Justice Farida Rabi’u Dan Baffa, da kuma Justice Musa Dahiru Muhammad.
Sannan kuma sauran su ne Justice Halima Aliyu Nasir, Justice Aisha Mahmud, Justice Adam Abdullahi, da kuma Justice Hanif Sunusi Yusuf.
A ɓangare guda kuma Alƙalan kotunan ɗaukaka ƙara na shari’ar Musulunci da aka naɗa sun haɗar da Khadi Muhammad Adam Kademi, da Khadi Salisu Muhammad Isah, sai kuma Khadi Isah Idris Sa’id, da kuma Khadi Aliyu Muhammad Ƙani.
Yayin da yake jawabi ga Alƙalan a wajen bikin rantsuwar da aka gudanar a ɗakin taro na Africa House dake gidan gwamnatin Kano, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce an yi naɗin ne a bisa cancanta, inda naɗin nasu y
Yanzu haka gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya rantsar da sabbin Alƙalai a matakan kotunan daban-daban na jihar ta Kano.
Hakan na zuwa ne ta cikin wata sanarwa da babban daraktan yaɗa labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a yau Juma’a, da aka aikewa manema labarai.
Sanarwar ta ce Alƙalan da Gwamnan Kano ya rantsar sun haɗar da Alƙalan Babbar kotun Jiha guda tara (9), da kuma Alƙalan kotun ɗaukaka ƙara na shari’ar Musulunci guda uku (4), bayan da hukumar kula da sharia ta kasa (NJC) da kuma majalisar dokokin jihar Kano suka amince da naɗin nasu.
Haka kuma waɗanda aka naɗa a matsayin alƙalan babbar kotunan Jihar sune, Justice Fatima Adamu, Justice Musa Ahmad, Justice Hauwa Lawan, da Justice Farida Rabi’u Dan Baffa, da kuma Justice Musa Dahiru Muhammad.
Sannan kuma sauran su ne Justice Halima Aliyu Nasir, Justice Aisha Mahmud, Justice Adam Abdullahi, da kuma Justice Hanif Sunusi Yusuf.
A ɓangare guda kuma Alƙalan kotunan ɗaukaka ƙara na shari’ar Musulunci da aka naɗa sun haɗar da Khadi Muhammad Adam Kademi, da Khadi Salisu Muhammad Isah, sai kuma Khadi Isah Idris Sa’id, da kuma Khadi Aliyu Muhammad Ƙani.
Yayin da yake jawabi ga Alƙalan a wajen bikin rantsuwar da aka gudanar a ɗakin taro na Africa House dake gidan gwamnatin Kano, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce an yi naɗin ne a bisa cancanta, inda naɗin nasu ya zama shaida da ke nuna ƙwarewar su ta fuskar shari’a, dama jajircewarsu wajen tabbatar da adalci da kuma doka da oda.
Gwamnan Kano ya kuma ce, “Haƙƙin da kuke ɗauka yana da yawa, kuma tasirin hukuncin ku ya kai ko’ina; Wannan nauyi ne da ke buƙatar ba wai kawai ƙwarewar shari’a ba har ma da zurfin fahimta, tausayawa, da jajircewa wajen kiyaye muhimman ƙa’idoji waɗanda aka gina tsarin shari’ar mu a kansu, “in ji Abba Gida-gida”.
Gwamna Abba Kabir ya ci gaba da cewa tun da aka kafa gwamnatinsa ta amince da mafi yawan buƙatu daga bangaren shari’a da ke da alaka da ƙudirin gwamnatin sa na raba madafun iko da ‘yancin kan ɓangaren shari’a, kamar yadda jaridar GTR Hausa ta rawaito.
Daga bisani dai Abba Kabir ya kuma buƙaci Alƙalan da su yi aikin su cikin tsoron Allah, tausayawa da jajircewa wajen yin hidima tare da bayyana kyakykyawan fata a gare su dangane da Wannan sabon nauyi da ya hau wuyan su.
Rahotanni sun bayyana cewar bikin rantsuwar ya samu halartar babbar Alƙaliyar alkalan jihar Kano, Mai shari’a Dije Aboki, da kuma Grandi Khadi na Kano, Khadi Tijjani Yusuf Yakasai, da Alƙalai da sauran jiga-jigan dake fannin shari’a daga bangarori daban-daban na ciki da wajen jihar Kano.
Dala Fm