Gwamnatin Edo Ta Dage Ranar Komawa Makaranta Saboda Karin Man Fetur

Spread the love

Gwamnatin jahar Edo ta dage ranar komawar daliban makarantun Sakarandire da Firamare sakamakon karin farashin kudin man fetur .

Gwamnatin jahar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren  ma’aikatar ilimi Ojo Akin-Longe, ya fitar a Benin ranar Asabar.

Idongari.ng, ta ruwaito cewa, a ranar 9 ga watan satumba 2024, aka sanya a matsayin ranar komawar daliban, amma saboda karin farashin fetur din aka dage zuwa wani lokaci anan gaba.

Dage ci gaab da karatun ya shafi makarantun gwamnati da kuma masu zaman kansu a fadin jahar.

DANDALIN KANO FESTIVAL

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *