Gwamnatin Kaduna za ta dasa bishiyoyi 20,000 a bana

Spread the love

Gwamnatin Jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya ta ce za ta dasa bishiyoyi 20,000 a 2024 a fadin jihar.

Kwamishinan muhalli da albarkatun ƙasa na jihar Abubakar Buba ne ya bayyana hakan yayin wani taron kwana ɗaya kan manufofin sauyin yanayi a jihar, taren da haɗin gwiwar kungiyar Save the Children.

Ya ce shirin wani yunkurin ne na rage tasirin sauyin yanayi da ake fama da shi a jihar da ma ƙasa baki daya.

Da take nasa jawabin babbar sakatariyar ma’aikatar Linda Yakubu wadda ta wakilci kwamishinan ta ce matuƙar ana son ɗorewar jihar Kaduna do dole a yi wani abu game da lamarin sauyin yanayi.

“Sauyin yanayi gaskiya ne kuma mun fara ganin tasirinsa a jiharmu. Za a gabatar da sabbin manufofi da za a rage tasirinsa a jihar.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *