Gwamnatin jihar Kano ta ce ta umarci lauyoyinta su bibiyi wata takarda da suka ce tana yawo a shafukanta sanda zumunta da ke cewa kotu ta bayar da umarnin rufe asusun gwamnati.
A cikin makon nan ne takarda ta ɓulla a shafukanta intanet wadda ake cewa, ta fito ne sakamakon wata buƙata da bangaren waɗanda aka yiwa rusau a masallacin idi suka shigar.
Sai dai ma’aikatar shari’ar jihar Kano ta ce har yanzu ba a basu kwafin takardar umarnin kotun ba.