Gwamnatin jihar Kano ta miƙa mutanen nan guda 76 ciki har da ƙananan yara fiye da 20 da shugaba Tinubu ya yi wa afuwa bayan kotu ta same su da laifin yi wa ƙasa cin amana bisa ɗaga tutar Rasha da suka yi a lokacin zanga-zangar matsin rayuwa ta watan Agustan 2024.
Gwamnatin ta Kano dai ta hannanta mutanen ga iyalansu bayan karɓar su daga hannu mataimakain shugaban ƙasar Najeriya, Kashim Shettima ranar 5 ga watan Nuwamba.
Gwamnatin jihar Kanon dai ta yi alkawarin ɗaukar nauyin karatun mutanen 76 tare da ba su jari, domin samar musu da madogara.