Gwamnatin Nijeriya ta nemi taimakon kasar Faransa kan matsalar tsaro

Spread the love

Gwamnatin Tarayya ta miƙa kokon bara na neman taimako da haɗin kan Faransa domin kawo ƙarshen matsalar tsaron da ta dabaibaye kasar.

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar ne ya bayyana hakan yayin wata ganawar sirri da ya yi da wasu ’yan majalisa da kuma jami’an hukumomin tsaron Faransa a Yammacin wannan Talatar.

Ministan a yayin taron wanda Gassillound Thomas ya jagoranci wakilan Faransa a Abuja, ya buƙaci su kawo wa Najeriya ɗauki domin dakile ayyukan ’yan ta’adda da masu garkuwa da mutane da sauran kalubalen tsaro da suka addabi kasar.

A cikin sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar tsaron Najeriya, Henshaw Ogubike ya fitar, ministan ya ce akwai bukatar a inganta alakar da ke tsakanin Najeriya da Faransa ta fannin kayan aikin soji da horar da jami’an sojin kasar.

Aminiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *