Gwamnatin Oyo ta yi barazanar ƙwace kadara ko ɗaure duk wanda ya ƙi biyan haraji

Spread the love

Gwamnatin jihar Oyo da ke kudu maso yammacin Najeriya ta gargaɗi masu harkokin kasuwanci da mazauna jihar a kan ƙin biyan haraji, inda ta yi barazanar ɗaukar matakin shari’a a kan mutum.

Shugaban hukumar tara kuɗaɗe ta jihar, Mista Olufemi Awakan ne ya yi gargaɗin a wata sanarwa da hukumar ta fitar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito a ranar Asabar.

Sanarwar ta ce lokaci ya yi da za a biya duk wani haraji da ba a biya ba, kamar yadda doka ta yi tanadi dukkanin wani mazaunin jihar ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na haraji.

Mista Awakan ya ce, biyan haraji ba zaɓi ba ne abu ne da ya zama wajibi kamar yadda yake a sashe na 24 na kundin tsarin mulki Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *