Gwamnatin Tarayya Ta tallafawa Manoman Citta Da Naira Biliyan 1.6

Spread the love

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta ware naira biliyan 1.6 domin tallafa wa manoman  citta a jihohin uku harda Babban Birnin Tarayya Abuja.

Babban sakataren asusun bunƙasa noman citta, na kasa NADF Mohammed Ibrahim, ne  ya sanar da haka a wajen wani taro da aka yi a jahar Kaduna .

ya ce Gwamnatin tarayyara  za ta raba wannan tallafi a karkashin Shirin bunƙasa noma na ‘GRATE’.

Ibrahim ya ce akalla manoman citta 15,000 ne cutar ‘Blight’ ya shafa a jihohin Kaduna, Filato, Nasarawa da Abuja a Kuma lokacin da kasar ke bukatar citta domin siyar wa a kasashen waje.

Sakamakon bincike da hukumar kididdiga ta NBS ta gabatar ya nuna cewa Najeriya ta samu kari a kudaden shiga a dalilin kasuwancin citta zuwa kasashen waje daga naira biliyan 4.6 a 2022 zuwa naira biliyan 10 a shekarar 2023.

Ibrahim ya ce tallafin da gwamnati ta bada za a yi amfani da su,  wajen Samar wa manoma ingantattun iri, maganin feshi da takin zamani.

A karshe ya ce  suna sa ran tallafin da gwamnati ta bayar  zai taimaka wajen bunƙasa noman a kasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *