Gwamnatin tarayya za ta hukunta likitocin dake da hannu a safarar Koda

Spread the love

Gwamnatin Najeriya ta bayar da tabbacin ɗaukan mataki kan likitoci da sauran mutanen da ke da hannu a harkar safarar ƙoda.

Jami’ar yaɗa labarai ta ma’aikatar lafiya ta ƙasar, Ms Patricia Deworitshe ce ta bayar da tabbacin cikin wata sanarwa da aka fitar jiya Laraba a Abuja, babban birnin Najeriya.

A cewar jami’ar, gwamnati ta sanar da ƙudirinta na ladabtar da duk wanda aka kama da hannu a safarar ƙoda bayan rahoton da jaridar Daily Trust ta wallafa kan yadda ake yin harkar a ɓoye.

Ta ce “ma’aikatar ta yi tir da irin wannan mummunar ɗabi’a ta safarar ƙoda kamar yadda rahoton na Daily Trust ya bayyana.

Kotu Ta Ƙi Amincewa Da Buƙatar Mawaƙi Kan Hana BBC Amfani Da Kiɗansa

Shugabannin kananan hukumomi uku sun fice daga APC zuwa NNPP mai mulkin Kano

Ma’aikatar lafiyar ta kuma tunatar da mutane game da sashe na 51 zuwa 56 na dokar lafiya ta ƙasa da ya haramta safarar ƙodar.

“Mutanen da suka ƙi bin dokar sun aikata laifi kuma za su iya fuskantar biyan tarar naira miliyan ɗaya ko zama gidan yari ko ma duka biyun.

Kotu ta aike da yar Tiktok Ramlat Princess gidan gyaran hali bisa zargin yada badala

Kaunar Murja Kunya ya ratsa cikin zuciya ta don haka ku Aura mun ita: Ustaz Assalafi

Ms Patricia Deworitshe ta ce hukumar kula da aikin likitoci ta Najeriya tana duba zarge-zargen da aka yi kan likitoci da suke wannan ta’adar.

Deworitshe ta ƙara da cewa kamata ya yi bayar da gudummawar ƙoda ya zama bisa masaniyar wanda zai ba da ƙodar tasa, kuma bisa shawarar likita.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *