Har Yanzu Ba Mu Ga ‘Ya’yanmu Ba — Iyayen ‘Yan Matan Jami’ar Gusau

Spread the love

Iyayen yan matan da aka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya ta Gusau a Jihar Zamfara, sun ce ba su da labarin sakin yayansu a hukumance.

Kafafen sadarwa musamman na intanet sun ruwaito cewa an saki sauran yan matan guda tara da suka rage a hannun yan bindigar.

A watan Satumbar 2023 ne dai yan bindiga suka kai hari gidajen yan matan da ke daura da jami’ar a Unguwar Sabon Gidaa birnin Gusau.

Mahaifin ɗaya daga cikin yan matan, Dokta Ibrahim Mai Unguwa ya bayyana wa Aminiya ta wayar tarho cewa shi dai har yanzu a kafafen sada zumunta yake ganin labarin an saki yayan nasu, har ma an damka su ga hukumomin tsaro.

Ya ce “Gaskiya babu wanda ya kirani daga makaranta ko hukumomin tsaro dangane da sakin yaran.

 

Wadanda Suka Kashe Dakarunmu Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu — Tinubu

Dan Majalissar Tarayya  Gwarzo Da Kabo Ya Kaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane 10,000 A Mazabarsa.

“Ni ma ta kafafen sada zumunta na ga ana cewa an saki yayan namu, sai kuma a bakin jama’ar gari da kai da ka kirani.
Dokta mai Unguwa ya ce zai fi kowa farin ciki idan ta tabbata an saki yaran, kuma yana rokon Allah Ya tabbatar da sakin yayan nasu.

Shi ma dai Alhaji Ibrahim Malami, mahaifin ɗaya daga cikin yan matan ya bayyana mana cewa ya ji kafar Labarai ta BBC ta bayyana cewa an sako biyar cikin yan matan da aka yi garkuwa da su, amma bai samu labarin daga hukumar makaranta ko hukumomin tsaron Najeriya ba.

A nasa bangaren, shugaban jami’ar, Farfesa Mua’azu Abubakar ya bayyana cewa,“ A kafafen sada zumunta na ga batun sakin yaran, amma ina da yakinin cewa hukumomin tsaro na yin duk abin da ya dace a matsayinsu, amma ba ni da labarin sakin yaran.”

Shi ma dai kakakin rundunar yan sandan Zamfara, Yazid Abubakar ya ce, ba su samu labarin sakin yaran ba.

AMINIYA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *