Hukumomi a Johannesburg za su sauya wa mutum 150 matsuguni bayan gobara

Spread the love

Hukumomi a Afirka ta Kudu na shirin sauyawa fiye da mutum 150 da suka tsira daga gobarar da ta lakume wani gini da aka yi ba bisa ka’ida ba a Johannesburg.

Gobarar da ta tashi ranar Lahadi, ta halaka mutum biyu tare da raunata karin hudu.

Gobarar ta kuma daidaita iyalai da dama da ke zaune a ginin cikin muhalli mara tsafta.

An kama wata mata saboda zargin tana da hannu a iza gobarar.

Tashin gobara a gine-ginen da ake yi ba bisa ka’ida ba abu ne da ya zama ruwan dare a Johannesburg.

Ire-iren gine-ginen galibi kan fada hannun miyagu da suke ba da haya ba tare da muhalli mai kyau ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *