Hukumomi a Ukraine sun ce harin da Rasha ta kai ranar Asabar, a Kudu da kuma gabashin ƙasar ya kashe mutane aƙalla sha ɗaya.
Jagoran gwamnatin yankin Zaporizhzhia ya ce harin makami mai linzamin da Rasha ta kai garin Vilniansk ya kashe fararen hula bakwai, ciki harda ƙananan yara biyu, ya kuma raunata wasu sha ɗaya.
Ivan Fedorov ya yi bayanin cewa harin ya kuma rusa gine-gine da dama a yankin.
A yankin Donetsk da ke Gabashi ma an kashe mutum hudu, a wasu hare-hare da aka kai ƙauyukan yankin.
Shugaba Zelensky ya ƙara jaddada kiran sa ga ƙawayen Ukraine, na neman tallafin makamai, ciki harda na tabbatar da tsaron sararin samaniya.
Tun da farko dai rundunar sojin Rasha ta ce ta mamaye wani yanki na birnin Donetsk, wanda ke kusa da garin Toretsk da ta daɗe tana neman ƙwacewa.