Rundunar ƴansandan jihar Kano tare da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro a jihar sun ɗauki matakin haramta bukukuwan hawan salla a Kano.
Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ya ce hukumomin tsaron sun ɗauki matakin ne sakamakon dalilai na tsaro.
Matakin na zuwa ne bayan da wata takarda da aka yi amanna daga fadar Sarki Muhammadu Sanusi II ta fito, ta yi kira da hakimai da su shiga birnin Kano domin gudanar da bukukuwan hawan Sallah.
Ko a lokacin bukukuwan ƙaramar sallah ma hukumomin tsaron jihar sun haramta hawan sallah, saboda bayanan sirrin da suka ce sun samu na wasu ”ɓata-gari” da ke son amfani da bukukuwan hawan sallar wajen tayar da zauen tsaye a jihar.
- Gwamnatin Tarayya Ta Alakanta Ambaliyar Ruwan Mokwa Da Rashin Ka’idar Gine-gine
- 2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu
”Kan haka ne hukumomin tsaron suka sake ɗaukar matakan haramta hawan babbar sallah , saboda wancan barazanar tsaron har yanzu yana nan”, a cewar sanarwar.
Rundunar ƴansandan ta ce an ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar masu ruwa da tsaki kan bayanan sirri da suka samu da ke nuna cewa akwai wasu ɓata-gari da ke shirin amfani da lokacin bikin hawan sallar domin tayar da fitina a jihar.