Jami’an tsaro sun gano bama-bamai da aka binne a Neja

Spread the love

Jami’an Tsaro a Jihar Neja, sun gano wasu bama-bamai da abubuwan fashewa da yawa a wurare daban-daban da aka binne a wasu yankunan jihar.

Wuraren da aka binne bama-baman sun haɗa da yankin Galadima-Kogo a Ƙaramar Hukumar Shiroro, yankin Mutun-Daya a Karamar Hukumar Munya, da yankin Gbeganu da ke Minna

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun ne, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Ya bayyana cewa an gano abubuwan fashewar ne yayin ayyukan yaki da ta’addanci tsakanin shekarar 2021 zuwa 2023.

A Galadima-Kogo, wani bam ya tashi a shekarar 2022, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wasu jami’an Hukumar Sibil Difens (NSCDC).

An ɓoye abubuwan fashewar ne a wurare daban-daban, amma tawagar ‘yan sanda tare da sauran hukumomin tsaro a jihar sun gano su, inji kakakin ‘yan sandan.

Abiodun, ya ƙara da cewa an lalata bama-baman a ranar 22 ga watan Agusta, 2024, a bayan Dutsen Zuma da ke Suleja.

Ya ce aikin ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin SP Mohammed Mamun, wanda ke kula da sashen lalata bama-bamai na rundunar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *