Jami’anmu ba su yi harbi a lokacin zanga-zanga ba – IGP

Spread the love

Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya ya ce babu jami’insu da ya yi harbi lokacin zanga-zanga.

Sufeton ya yi wannan maganar ne a lokacin ya ke kare zargin da aka yi wa jami’ansu na yin harbi a yayin zanga-zangar matsin rayuwa da ‘yan kasar ke yi.

Ya ce duk jami’in da aka gani da bakin kaya a ranar zanga-zanga ba jami’insu ba ne saboda ba kayan da suka saba sanyawa suka sa ba a ranar.

Sannan ya ce,sun kama masu dinka tutocin kasashen waje don su kai su wajen masu daukar nauyinsu.

A jihar Kano kuwa ‘yan sanda sun ce sun fara yi wa wadanda suka kama sharia.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *