Jami’in Kwastam Ya Fadi Ya Mutu A Zaman Majalissar Dokokin Nigeria

Spread the love

Wani jami’in hukumar kwastam ta Najeriya ya mutu yayin halartar zama don amsa tambayoyi a majalisar wakilai.

Wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin yada labarai na majalisar Akin Rotimi ya fitar a ranar Talata, ta ce jami’in ya “gamu da yanayi na rashin lafiya nan take” yayin amsa tambayoyi, al’amari da ya faru da misalin karfe 1 na rana.

Ya ce, “Mun kaɗu matuka da mutuwar jami’in na kwastam wanda ya halarci zauren majalisar.

Ya ce jami’an lafiya a asibitin majalisar wakilan sun yi kokari wajen bai wa jami’in kulawa, amma sai rai ya yi halinsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *