‘Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya

Spread the love

Kwamitin Kwamishinonin Lafiya na Arewa maso Gabashin Najeriya ya nemi tallafi daga Hukumar Raya Yankin Arewa maso Gabas, (NEDC) da ta tallafa wajen rage yawan mace-macen mata da jarirai a shiyoyin ƙasar.

Ya ce kashi 30 cikin 100 na mace-macen mata masu juna biyu da jariran da aka haifa a duniya suna faruwa ne a Najeriya.

Shugaban kwamitin, Farfesa Baba Mallam Gana ya bayyana hakan ne a wata ganawa da shugabannin hukumar NEDC kan hanyoyin inganta harkar lafiya a yankin.

Ya ce matsalar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai da sauran matsalolin da suka shafi mata masu juna biyu da ke dagula harkar lafiya a yankin arewa maso gabas na da matukar muhimmanci a magance su.

An kuɓutar da matar basaraken da aka kashe a Kwara tare da kama mutum 13

Kisan Nafi’u: Shari’ar Hafsat Chuchu Ta Samu Tsaiko.

“Bangaren kiwon lafiya a yankin Arewa maso Gabas na cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu, musamman idan aka yi la’akari da yanayin mata da jarirai da yaran da ake haifa.

“Hukumar NEDC ta yi ayyuka da yawa a fannin kiwon lafiya, amma a gaskiya, a yanzu mun fi buƙatar hukumar.

“Mu na da masaniya kan ayyukan hukumar, kamar inganta asibitin ido zuwa matsayin kasashen duniya. Yanzu, za mu yi aiki tare da Hukumar NEDC don inganta harkokin kiwon lafiyar al’ummar Arewa maso Gabas,” in ji Gana.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *