Kisan Nafi’u: Shari’ar Hafsat Chuchu Ta Samu Tsaiko.

Spread the love
Hafsat, mijinta Dayyabu Abdullahi , Malam Adamu

Shari’ar zargin Hafsat Suraj (Chuchu) da wasu mutane uku kan zargin kashe wani mutashi mai suna Nafiu Hafiz da ke gaban Babbar Kotun Jihar Kano ta samu tasgaro.

Shari’ar da ke gaban Mai sharia Zuwaira Yusuf ta babbar kotun jahar Kano, da ke zamanta a titin Miller ta samu tsaiko  ne sakamakon rokon da bangaren wadanda ake zargi ga kotun ta sanya musu wata rana da za a karanta wa wadanda ake kara takardar tuhumarsu.

Wadanda ake tuhumar sun hada da Hafsat Chuchu da mijinta da mai gadinsu da kuma malamin da ake zargi da yi wa gawar Nafiu wanka.

An taba gurfanar da su gaban kotun Majistare da ke zamanta a ’Yankaba karkashin jagorancin Mai Shari’a Hadiza Abdurrahman inda ake tuhumar Hafsat Chuchu da kisan Nafiu Hafiz, sauran mazan kuuma ake tuhumar su da laifin boye gaskiyar dalilin rasuwar Nafiu.

Yan Najeriya su guji murnar wuce iyaka idan Eagles suka doke Bafana Bafana’

Shugaban karamar hukumar Nasarawa ya koma NNPP Kwankwasiyya a Kano

Sai dai lokacin da Gwamnatin Kano ta fara gurfanar da su, dukkansu sun amsa laifin da ake tuhumar su da aikatawa.

Daga bisani aka sanya Talata 6 ga watan Fabrairu, 2024, don sake gurfanar da su a gaban Babbar Kotun Jihar, amma gurfanarwar ba ta yiwu ba.

Tunda farko bangaren masu gabatar da kara karkashin jagorancin Barista Aisha Mahmud sun nemi kotun ta yarje mu su, don musanya takardar karar da wata sabuwa, kasancewar sunan wanda ake zargi na hudu, ba ya cikin tsohuwar takardar rokon da kotun ta amince da shi.

Amma bangaren masu kariya karkashin jagorancin Barista Huwaila Ibrahim Muhammad sun nemi kotun ta sanya wata rana don sake gurfanar da wadanda ake zargin a gabanta domin su da wanda suke karewa na hudu su samu damar yin nazarin takardar karar.

Kotun ta sanya ranar Alhamis 8 ga watan Fabarairun 2024 don gabatar da wadanda ake tuhumar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *